Muna Fama Da Talauci .. inji Sakataran APC Kaduna

Jam’iyyar APC ta jihar Kaduna ta koka dangane da yadda talauci yayi mata katutu wanda hakan yana haifar musu da matsaloli wajen tafiyar da aikinsu a jihar 

Bayanin haka ya fito ne daga bakin sakataran jam’iyyar Yahaya Baba Pate,  yayin da yake gabatar da jawabinsa a wurin taron shugabannin jam’iyyar wanda ya gudana a jiya.

Baba Pate, ya bayyana cewa  jam’iyyar bata samun tallafi daga wurin  ‘ya’yan jam’iyyar masu rike da madafun iko inda yace suna ji a jikinsu na rashin kudi.

Ya bayyana cewa masu rike da mukamai daga karamar Hukumar zariya sune kadai suke Tallafawa jam’iyyar, a cewarsa, sauran basa tabuka komai 

Ya kuma bayyana cewa jam’iyyar su ta samu nasarori da dama a cikin shekara daya.

Leave a comment