Gwamnatin Kaduna Zata Tura Mata  300 Karatun  Likita  Kasar Cuba 

A kokarinta na bunkasa harkar  ilimi da lafiya  a jihar kaduna, gwamnatin jihar ta bayyana cewa  zata tura dalibai Mata guda 300 Karatun Likita a Kasar Cuba domin samo ilimin Likita.

Gwamnatin tace za’a Fara tura daliban Kasar Cuba ne daga  farkon zangon karatu na   shekara 2018/ 2019 wanda Kuma Gwamnatin ta kammala duk wani shirin da Suka kamata  Akan tafiyar daliban.

Bayanin hakan ya fito ne daga bakin  gwamnan jihar kaduna Nasiru Ahmed El-rufai, a wani rubutu  da ya wallafa  a shafinsa na TWITTER inda yace a duk  shekara Gwamnatin zata rinka  tura dalibai  Mata 300 zuwa Kasar Cuba domin Karatun Likita,  a cewarsa hakan Zai Kara sanyawa  a samu yawaitar Mata likitoci  a asibitocin jihar kaduna baki daya.

Hakazalika,  gwamna El-rufai ya ce Gwamnatin jihar kaduna zata Gina magana’antar  sarrafa  magunguna a cikin  jihar wanda ‘yan Kasar Cuba ne zasu hada  hannu  da gwamnatin wajen gina  magana’antar.

 A cewarsa, gwamnatin sa zata sayo  magunguna  daga Kasar Cuba masu yawa wadanda za’a  raba a daukacin asibitocin jihar domin tabbatar da cewa ta cika alkawarin ta na inganta Harkar lafiya a fadin jihar baki daya.

Leave a comment