Kungiyar NULGE Ta Bukaci Ma’aikatan Kananan Hukumomin Kaduna Da Su Koma Bakin Aiki

Shugaban kungiyar ma’aikatan kananan hukumomi na Jihar Kaduna (NULGE),Kwamared Rayyanu Isyaku Turunku,ya bukaci daukakin ma’aikatan kananan hukumomin Jihar da su kasance a bakin aikin su,musamman wadanda suke kananan hukumomin Kajuru,Chikun,Kaduna ta Arewa,Kaduna ta Kudu,da Igabi, da aka sanya doka saboda rikicin da ya faru a makon jiya .
Kwamared Rayyanu Turunku ya yi wannan kiran ne a yau, a Kaduna,a lokacin da yake tattaunawa dà manema labarai a Kaduna .
Ya ce tun da zaman lafiya ya fara dawowa wandà a sabili da ganin haka ya sa gwamnatin Jihar Kaduna ta sassàuta doka ya koma daga karfe 6:00am zuwa karfe 5:00pm,ya sa ya yi wannan kiran .
Shugaban iya ce muddin gwamnati ta ga al’ummar jihar sun yarda, sun rugumi juna, sun yarda su zauna lafiya,to za ta rika sassauta dokar har ta cire shi gaba daya .
Ya yaba wa ma’aikatan kananan hukumomin saboda rawar da suka taka wajen tabbatar da rikicin bai yadu ba a sauran daukakin kananan hukumomin jihar 23,sannan sun kuma sun yi kokari zaman lafiya ya fara dawowa yadda ya kamata .
Haka ya jinjina wa gwamnan Jihar Kaduna,Mallam Nasir Ahmed El-Rufa’i saboda matakan gaggawa da ya dauka a lokacin da rikicin ya barke .
Sannan ya bukaci al’ummar Jihar Kaduna da su rungumi akidar zaman lafiya domin samun ci gaba .
Haka ya ce a halin rashin zaman lafiya babu wani ci gabà da za a samu sai koma baya .

Leave a comment