Zamu gina ‘kasa kamar yadda muka yi a Lagos da Borno – Sanata Shettima

Sanata Kashim Shettima

From Ibraheem Hamza Muhammad

Sanata Kashim Shettima ya jaddada cewa ‘kasar Najeriya zata mori romon mulkin dimokradiya idan aka zabi Asiwaju Bola Ahmed Tinubu na jam’iyyar APC a matsayin Shugaban ‘Kasa a zaben da ke gabatowa.

A takardar sanarwa da kakakin kwamitin APC mai neman a za’bi Bola Ahmed Tinubu da Sanata Kashim Shettima, Mista Bayo Onanuga ya fitar, ta ce, Sanatan ya furta haka ne a ranar Litini a Legas yayin da ya wakilci Tinubu a taron shekara-shekara na Kungiyar Lauyoyi ta kasa. Inda ya ce, aikin gani-da-ido da Tinubu da Shettima suka aiwatar a Lagos da Borno ya zama manuniyar cewa su masu aiki tukuru ne.

Tsohon Gwamnan na Borno ya ce, duk da yanayin rashin tsaro a Arewa-Maso-Yamma yayin da yake mulki, ya taka rawar gani a fannin ilmi.

Sanata Shettima ya kara da cewa, “Jama’a suna da alhakin su yabawa mai aiki a maimakon mai yawan dogon turaci.

” Ya dace Jama’a su bi wanda ya san hanyar zuwa ga daukaka, domin in an zabe mu, a ranar farko za mu fara aikin yalwata tattalin arzikin kasa, samar da yanayi mai alfanu da kuna inganta tsaro.

“ Da Tinubu da ni gwaraza ne da muke son gina ‘kasa: Alal misali, ana iya zuwa Borno don gani-da-ido yadda na gina makarantu, sannan na inganta samar da ilmi gadan-gadan duk da ana yaki da masu dauke da makamai a lokacin.

” Ba za mu yi ‘kasa a gwuiwa ba wajen kambana ayyukan da muka yi a jihohinmu don ciyar da jama’a su sami bunkasa.” .

” A takaicen-takaitawa, mun kuduri aniyar yin jagoranci na gari. ” A cewar Sanata Kashim Shettima.

Leave a comment