A kokarin da gwamnatin jihar kaduna kayi na Samar da taki ga Manoman jihar, Manoman karamar hukumar Birnin Gwari suna Zargin jami’an ma’aikatan aikin gona ta jihar da Karkatar da Takin da gwamnatin jihar ta warewa Manoman karamar hukumar.
Binciken da wakilinmu ya gudanar a karamar hukumar birnin Gwari ya tabbatar da cewa Gwamnatin ta aiki da taki tirela Biyu a makon da ya gabata Amma an Karkatar da takin zuwa ga ‘yan kasuwa maimakon a bawa Manoman karamar hukumar.
Manoman birnin Gwari sunce gwamnatin jihar kaduna ta bawa Manoman karamar hukumar Taki tirela 70 wanda daga ciki an Kai musu tirela 7 wanda a makon da ya gabata an tura tirela biyu Amma baikai ga Manoman karamar hukumar ba.
Manoman sunce duk badakalar takin da gwamnatin jihar ta warewa Manoman karamar hukumar Akwai hadin baki da manyan jami’an ma’aikatan aikin gona ta jihar da wakilan da ma’aikatan sarrafa Taki ta tura karamar hukumar birnin Gwari. Akan hakan sun bukaci gwamnatin da ta tabbatar ta Binciki lamarin domin kawo musu dauki.
Sai dai mai Kula da dakin da ake ajiye takin wanda kamfanin takin ta turo a Kula da takin mai suna Malam Adamu shine Ke Karkatar da takin zuwa ga yan kasuwa maimakon a bawa Manoman karamar hukumar birnin Gwari.
Mun nemi jin ta bakin malam Adamu domin sanin halin da takin Manoman karamar hukumar yake, inda yace shi ” banda masaniyar komai Akan takin saboda Ni Babu hannu Na a ciki” Inji shi.
Da yawan Manoman karamar hukumar birnin Gwari sun sayi takin Kuma sun bada kudinsu Amma ba’a basu takin ba har ya zuwa yanzu Babu labarin takin inda Suka ce duk manomin da ya biya kudin takin basa samu. Binciken mu ya tabbatar da cewa takin da gwamnatin jihar ta warewa Manoman karamar hukumar birnin Gwari Ana sayar da shi a kasuwa.
Mun nemi jin ta bakin maaikatar aikin gona ta jihar kaduna domin jin ta bakin su, inda daraktan aikin gona ta ma’aikatan mista Bege, inda yace Shima ya samu labarin hakan Yana mai cewa Babu shakka sun tura tirela biyu Amma Ance bai Kai ga Manoman ba yace Zai bincika lamarin.
Manoman karamar hukumar birnin Gwari suna Kira ga gwamnan jihar kaduna da taimaka musu wajen ganin yakawo musu gudummawa domin tabbatar da cewa an kawo musu takin da Suka biya kudinsu.