Shugaban kasa muhammadu Buhari, ya gana da sarakunan gargajiyar kasar a fadar gwamnatinsa da ke babban birnin tarayya Abuja.
Wannan ganawa itace ta farko tun bayan dawowarsa daga kasar birtaniya duba lafiyarsa. Shugaban ya bayyana cewa sarakunan gargajiya suna taka rawar gani wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro a fadin kasar nan baki daya.
Sarakunan gargajiya da dama suka halarci ganawar da shugaban kasar, cikin su kuwa hard a mai alfarma sarkin musulmi Abubakar Sa’ad da kuma sarkin Kano Muhammadu Sanusi da Sarkin Zazzau da dai sauran manyan sarakunan gargajiya daga sassa daban-daban na fadin kasar nan