GARGAJIYA: Gwamnatin Jihar Kano Ta Rufe Asibitin Maita

Daga Nasiru Salisu, Kano

Hukumar kula da asibitoci masu zaman kansu ta jihar Kano da hadin gwiwar hukumar karbar korafe-korafe da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano sun rufe wani asibitin Maita da aka bude a nan Kano.

Asibitin wanda Chiroman sarkin mayun Kano, Alhaji Yahya Ali ya bude a garin Gano dake karamar hukumar Dawakin Kudu, ana kwantar da marasa lafiya tare da lura dasu ta hanyar maita.

Wasu majinyata da aka samu a asibitin sun bayyana cewa ana kafa musu kusa tare da zuko ruwa daga cikinsu da sunan yi musu magani.

Leave a comment