Gwamna  Mai Mala Buni  Alheri Ne Ga Al’ummar Jihar  Yobe– Yusuf Musa 

Alhaji Yusuf Musa lokacin da ya amshi lambar yabon

Daga Shehu Yahaya

Jigo a Jam’iyyar APC ya bayyana gamsuwarsa dangane da  kokarin gwamnan jihar Yobe Mai Mala Buni yake tallafawa kaukacin al’ummar jihar ta bangarori daban-daban a fadin jihar.

Bayanin Hakan ya fito ne daga bakin Alhaji Yusuf Musa, a zantawarsa da manema labarai a Kaduna Jim kadan bayan kungiyar ‘Yan Jarida ta Arewa ta karramashi da lambar yabo bisa irin gudummawar da yake bayarwa wajen ci gaban jihar Yobe da Arewacin Nijeriya baki daya.

Gwamna Mai Mala Buni na jihar Yobe

Alhaji Yusuf Musa, wanda Yana daga cikin ‘ Yan kwamitin rabon tallafin kayan  cire tallafin man fetur na jihar, yace gwamnatin Mai Mala Buni  budaddiyar gwamnati ce da kowa zai shaida.

Alhaji Yusuf,  wanda shine shugaban kamfanin Yusufana, yace gwamnatin Yabe ta Bawa  bangaren lafiya da na ilimi muhimmanci sosai, sannan ta  samar da ruwan sha da karfafa wa mata da matasa, domin duk matsalar jihar ya san yadda zai magance ta.

“Gwamnatin Mai Mala Buni tana  tallafawa matasa mata da maza  domin ana basu  kaso mai tsoka. Sannan iyaye mata da suke cikin gida ana taimaka musu   wajen samar musu  da kananan sana’o’i da za su dogara da su,” inji sh

Shugaban yace  a bangaren tsaro, yayi dukan mai yiwuwa wajen ganin ya sake daidaita sha’anin tsaron ya kuma bai wa jami’an tsaro damar gudanar da aikinsu yadda ya kamata.

Akan Hakan ya yaba da kokarin kafafen lada labarai bisa irin gudummawar da suke bayarwa wajen wayar da kan al’umma akan lamuran yau da kullum. Ya kuma godewa qungiyar ‘Yan jarida ta Arewa da suka karramashi bisa gudummawar da yake bayarwa wajen bunkasa rayuwar al’umma baki daya.

Leave a comment