YAKI DA ‘YAN TA’ADDA: Gwamna  Dauda Ya Kaddamar Da Askarawan Zamfara

.… Babu Sulhu Da ‘Yan Ta’adda- Gwamna Radda

Daga Shehu Yahaya

Gwamna Dauda Lawal  na jihar Zamfara ya kaddamar da rundunar Sakai wace akewa lakabi da Askawaran Zamfara, 2,646.

Da yake kaddamar da jami’an tsaron sa kai, a Gusau,  gwamna Dauda ya bayyana cewa, samar da tsaro yana daga cikin kudirorin da dauka domin bunkasa ci gaban jihar  Zamfara.

Yace sun yiwa al’ummar jihar alkawari a lokacin yakin neman  zaben zasu taimaka wajen harkokin tsark wanda , cewarsa, “yau gashi Allah ya nufemu da kaddamar da rundunar Askawaran Zamfara wadanda da zasu taimaka ma jami’an tsaro wajan kauda “Yan Bindiga da suka addabi Jihar”

“Da yardar Allah zamuyi iya bakin kokarin mu tare da wadannan Askawaran dan ceto alumar Zamfara daga halin rashin tsaro” inji shi.

A nasa jawabin Babban bako Mai jawabi Gwamnan Jihar Katsina  Diko  Umar Radda,  ya bayyana cewa, wannan shiri na kaddamar da ‘yan sakai dan fatatakar “Yan ta’adda shiri ne na gwamnoni bakwai  na yankin Arewa Mason yamma.

Gwamna Radda yace “babu sulhu tsakanin mu da ‘yan Bindiga sai fafatawa,  yanzu gwamnan Zamfara ya tarbi yankin sa nima haka wannan ya tabbatar da cewa lallai batun sulhu babu shi har abada sai munga bayin ‘yan ta’adda da yardar Allah” 

Shima a nasa jabawabin  Janar Ali Gusau mai murabus, ya bayyana cewa “wannan rundunar Askawaran Zamfara an samar da itane domin  kare rayukan mu da dukiyoyin mu, bisa doka saboda  haka zasuyi aiki kafada da kafada da jami’an tsaro domin  samun nasara aikin su”

Leave a comment