Kungiyar NAPPMED  Zata Kawo  Karshen Sayar  Da Muyagun Kwayoyi A Kano

 Kungiyar masu sayar da magunguna ta kasa  (NAPPMED)  reshen  jihar Kano ta bayyana kudirinta  na tallafawa gwamnatin jihar  Na kawo karshen Matsalar masu sayar da  muyagun kwayoyi a fadin jihar. 

Kungiyar tace A shirye take Da ta Magance Matsalar yawaitar masu sayar da magungunan  Maye a jihar Kano wanda hakan Yana daga cikin abubuwan da kungiyar ta sanya a gaba. 

Bayanin hakan ya fito ne daga bakin  Malam Dahiru  Abdullahi Matazu, wanda shine  uban kungiyar masu sayar da magunguna ta jihar kano, (NAPPMED) yace “Muna bakin kokarinmu na kawo karshen Matsalar masu shaye-shayen muyagun  kwayoyi wadanda ake sayar da su a shaguna. 

Ya Kara da cewa yanzu Haka kunhiyarsu ta kafa wani kwamiti da Zai rinka Shiga shaguna suna duba irin magungunan da ake sayarwa da zimmar bankado masu sayar da muyagun kwayoyi a kasuwar sabon gari. Acewarsa tuni wannan kwamitin ya Fara kama irin wadannan masu shagunan Kuma suna karbar  magungunan. 

Yace baya ga kama masu sayar da muyagun kwayoyi suna kwato magungunan da basu da inganci wadanda ake sayarwa jama’ar jihar, inda yace Idan sun kama irin wadannan magungunan suna Mika su ga jami’an tsaro wasun su Kuma su rabawa masu cutar amosanin jini (sicle cell)  kyauta.

Malam Dahiru,  ya ci gaba da cewa  “Muna so mu bawa Gwamnatin jihar Kano goyon baya domin ganin an Magance Matsalar yawaitar masu shaye- shaye.

“Muna bukatar  gwamnatin jihar Kano data hada hannu da malaman addini  da kungiyarmu wajen Magance Matsalar, saboda Haka mu a shirye muke muyi  aiki da Gwamnati”inji Matazu. 

 Duk wanda baya sayar da magani  a kasuwa sabon gari to baya tare da mu saboda Haka duk wanda Ke sayar da magani a kasuwar sabon gari shine mamban  mu” a cewarsa 

Leave a comment