Nayi Nadamar Gudummawar Da Na Ba Gwamnatin Buhari- Mawaki Rarara

Rarara a Jawabinsa yayin Taron Manema labarai a Kano

Daga Muhammad Abdullahi

Shahararren mawakin APC Dauda Adamu Abdullahi wanda aka fi sani da Rarara ya ce gwamnatin da ta gabata ta tsohon shugaban kasa Muhammad Buhari ta lalata kusan kowane bangare na Nijeriya.

A wata ganawa ta musamman da manema labarai a Kano, ya ce ya ba gwamnatin ta Buhari shawarwari daban-daban na yadda za a inganta ayyuka rayuwar al’umma, amma ba ta dauki shawara ko daya daga bangare na ba inda yace yayi nadamar irin gudummawar da ya Bawa gwamnatin Buhari.

Mawakin da ya yi jawabi mai kama da ya dawo rakiyar gwamnatin da ta shude, ya nuna kamar yana nadamar irin goyon bayan da ya bata

Ya yi karin hasken cewa bai samu sisin-kwabo a gwamnatin Buhari ba, ya kara da cewa duk wanda ya ke da hujjar cewa ya samu kudi gwamnatin Buhari ya zo ya nuna.

Ta fuskar ba da gudunmuwa a wajen kafa sabuwar gwamnatin Tinubu kuwa, mawaki Rarara, ya ce tsoffin gwamnonin Katsina Aminu Masari da na Kano Abdullahi Ganduje ne kadai za su iya daga masa yatsa wajen bada gudunmawa har Tinubu ya sami nasara.

Sai dai Dauda Adamu ya yi karin hasken cewa akwai makiya Tinubu da aka nada mukamai daban-daban a gwamnatinsa.

Leave a comment