Majalisar Dattawa Zata Gayyaci Shugaban Bankin Manoma Kan Badakalar Kudin Manoma 

Dakta Maina A Tsaye A  Harabar
Majalisar Tarayya t
Ta
Kasa

Daga Shehu Yahaya

Majalisar dattawa ta amince zata gayyaci Shugaban Bankin Manoma  ta Nijeriya Alwan Ali Alhassan da ya bayyana a gaban kwamitin Kula da yaki da cin hanci da rashawa domin  amsa tambayoyi akan  badakalar kudaden manoma.

‘Yan majalisar Datawan sun cimma daukar wannan mataki ne a yayin zamansu da  Shugaban Kungiyar yaki da cin hanci da rashawa ( Anti Corruption Corps)  Dakta Maina Abdullah Gimba a Abuja.

A wata sanarwa da aka rabawa manema labarai a Kaduna mai dauke da sa hannun Darakta  Janar Ma kungiyar  ta  ACC Dakta Maina Abdullah Gimba, yace kungiyarsu ta zauna da sakataran  kwamitin majalisar Dattawa akan  amsar koken al’umma  inda suka amince zasu gayyaci Shugaban Bankin Manoman bisa korafe- korafe na karkatar da kudin manoma sama da biliyan 10.

Dakta Maina Tare Da ‘Yan Majalisar Datawan A Abuja

Dakta Maina Abdullah Gimba, ya kara da cewa  kungiyarsu ta bankado badakalar kudi na manoma da bankin bisa jagorancin Shugabanta Alwan Ali Alhassan yayi lamarin da ya Sanya suka kai kararsu zuwa majalisar domin gudanar da bincike da kuma daukar matakan da suka dace akan lamarin.

Akan Hakan sun bukaci bayan kammala binciken da ‘yan majalisar, gwamnati ta  tsige shugaban bankin manoman wanda a cewarsa,  suna da tabbacin cewa an karkatar da kudadan manoman kasar nan.

A zantawarsa da wakilinmu ta wayar tarho,  Barista Kaka Lawan Shehu,  ya tabbatar da cewa zasu gayyaci Shugaban bankin manoman domin ya kara gurfana a gaban kwamitin Karo na biyu domin amsa zarge- zargen da ake masa akan kudadan manoman Nijeriya. 

Leave a comment